Connect with us

News

EDIL-KABIR: Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutu A Makarantun Firamare Dana Sakandire A Fadin Jahar.

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Gwamnatin jihar Kano ta umarci dukkan makarantun firamare da na gaba da firamare da ke jihar da su ba da  hutun Edil-Kabir daga ranar Juma’a 14 ga watan Yuni, 2024 zuwa Litinin 24 ga watan Yuni, 2024.

Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta kara da  cewa, a saboda hakane ana bukatar iyaye da masu kula da daliban da ke makarantun kwana da su dauki ‘ya’yayenssu a safiyar Juma’a 14 ga watan Yuni, 2024.

Ya kuma yi Kara da cewa duk sauran tsare-tsaren Dake cikin jadawalin kalandar karatun makaranta ta 2023/2024 wadanda suka hada da ranar hutu na nan yadda yake a tsare.

Sanarwar ta ruwaito cewa Kwamishinan Ilimi, Alhaji Umar Haruna Doguwa ta bakin Daraktan wayar da kan jama’a yana kira ga iyaye da masu kula da su da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun dawo makaranta ranar da aka sanya dan cigaba da karatu.

Advertisement

Kasancewar za’a dauki matakin ladabtarwa a kan duk daliba ko dalibin da ya kasa komawa bisa ga sharuddan da aka gindaya a kwanan wata.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending