Connect with us

News

Hukumar NDLEA Ta Kama Dillalan Ƙwayoyi Fiye Da Mutum 1,344 A Katsina

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta ƙasa NDLEA reshen jihar Katsina ta bayyana kama mutane 1,344 da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da masu safarar sauran haramtattun kayayyaki a shekarar da ta gabata.

Advertisement

Kwamandan hukumar na jihar Katsina, Hassan Abubakar, shi ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis.

Daruruwan Mutane  Sun Banka Wa Wani Mutum Wuta Bisa Batanci Ga Al-Qur’ani

Ya kuma ƙara da cewa hukumar ta kama jimillar kilogiram 1,319.258 na kayan maye daban-daban, da suka hada da Cannabis Sativa, kayan maye, da kuma sauran magungunan da aka hana Safarar su.

Advertisement

Channels TV ta ruwaito cewa Tattaunawar ya gudana ne a yayin da ake gudanar da shirin tunawa da ranar yaki da shan muggan ƙwayoyi da safarar su na majalisar ɗinkin Duniya.

Kwamandan ya ƙara da cewa, rundunar ta yi shirye shirye akan wayar da kan mutane sama da 56,000, tare da baiwa mutane 136 shawara, ta kuma yankewa 107 hukunci, tare da gabatar da sabbin kararraki 120 .

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending