Connect with us

News

Siyasa Ta Lalata Mana Zamantakewa  Har Murna Ake Idan Musifa Ta Samu Mutum  —Barista Ishaq

Published

on

Malamin Addinin musulunci, Barista Ishaq Adam

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Wani Malamin Addinin musulunci, Barista Ishaq Adam, ya bayyana rashin jin dadinsa akan yadda al’ummar musulmi ke murna idan wata musifa ta afkawa dan uwansu, kawai saboda saɓanin ra’ayin kwallon ƙafa, ko siyasa ko wata mu’amala ta yau da Kullum .

Barista ya bayyana haka ne cikin wani bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook  na Karatuttukan Malaman Musulunci.

Advertisement

Inda ya bada misalin da sace mahaifiyar mawaƙin siyasa ne Dauda Adamu Rarara, da yace ya ga wasu sai murna suke yi, wanda hakan ba koyarwa Addinin musulunci bane,

Haka zalika ya ce a Addinin musulunci ana so duk abinda ya samu musulmi to dan uwansa musulmi yaji cewar kamar shi abin ya shafa.

Advertisement

Malamin ya ƙara da cewa, tsarin mulkin Demokradiyya ya sanya abubuwa sun lalace,

Wanda kamata yayi idan wata musifa ta samu mutum, a taimaka masa ko da addu’a ne, domin babu wanda ya tsira daga shiga irin wannan jarabawa.

Advertisement

 

 

Advertisement

NasaraRadio

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending