News
An Tarwatsa Masu Fasa Shaguna A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an tsaro sun tarwatsa gungun wasu matasa da ke kokarin fasa shaguna su kashe kayan jama’a a safiyar Alhamis a Jihar Kano.
Jim kadan da fara zanga-zangar tsadar rayuwa a Kano ne matasan suka yi wa wani kafafen shago dirar mikiya da sunan kwasar ganima.
Gwamnan Kano Ya Sanar Da Naɗa Sabbin Hukumomin Zartarwa A Manyan Makarantun Jihar
Amma jami’an tsaro sun dakile yunkurin sun kuma fatattake su.
Haka zalika Jaridar INDA RANKA ta ruwaito cewa sai da Jami’an tsaro na Bijilanti suka fatattake masu matasa da ke kokarin fasa shaguna su kashe kayan jama’a a a kan titin Yan Awaki dake Unguwa Uku dake karamar Hukumar Tarauni.
Advertisements
