Connect with us

News

Jami’an Tsaro Sun Ruga Da Sun Zama Karnukan Farautar Gwamnatin Tarayya— Kungiyar kwadago Ta NLC

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta ce  Jami’an Tsaro sun ruga da sun zama karnukan farautar gwamnatin tarayya a wannan lokacin.

Advertisement

Sakataren tsare tsaren  na kungiyar kwadago ta Najeriya NLC   Kwamared Nasir Kabir ne ya baiyyana hakan ya na mai cewa  yanzu rundunar  Yan Sanda a  Najeriya sun ruga da sun zama Karnukan Yan Siyasa.

Kwamared ya ce a yanzu babu wani girmama Dumukradiyyya da Gwamnatin Tarayya take ikirarin cewa tanayi duba da yadda Gwamnatin ke kama Shuwagabanni fararen Hula.

Advertisement

Kwamared Nasir Kabir ya bayyana haka ne a hirarsa da kafar yada labarai ta DCL HAUSA bayan kama Shugaban kungiyar kwadagon  Joe Ajaero da kuma afka wa ofishin ƙungiyar kare haƙƙi da sa-ido kan gwamnati, wato SERAP.

Kwamared ya ce shi tabbas bayyi mamakin kama Shugaban kungiyar Kasa  ba  tunda dai Jami,an Tsaro sun ruga da sun zama yan amshin Shata.

Advertisement

Mun umarci Jami,an tsaro dasu sake mana Shugaban mu idan Kuma hakan ɓata yiwuba tom zamu umarci dukkanin shuwagabannin kungiyoyin kwadago na jihohin 36 dasu zauna a shirin ko ta kwanana domin zamuyi yajin Aikin da ba’ata bayinsaba a Najeriya,Inji sa

Jaridar INDARANKA ta ruwaito cewa safiyar yau Litinin ce hukumar Yan Sandan farin Kaya ta DSS ta kama Shugaban kwadagon Joe Ajearo a filin Jirgin sama dake Abuja zai tafi Kasar Landon domin bikin wayar dakan Yayan kungiyar na Kasashen Duniya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending