News
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Litinin A Matsayin Ranar Hutu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin tarayya ta bayyana Litinin 16 ga watan Satumbar da muke ciki a matsayin ranar hutun Maulidi, don karrama bikin zagayowar ranar haihuwar Annabin tsira Muhammad (S.A.W).
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan, a madadin Gwamnatin tarayya inda yayi amfani da damar wajen taya al’ummar musulmi na gida Najeriya dana kasashen ketare murnar wannan biki mai alfarma.
Sojoji Sunyi Nasarar Kashe ƙasurgumin Dan Bindigar Nan Daya Addabi Arewacin Nageriya
Ministan ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su yi amfani da lokacin wajen yada halayen nagartu tsakanin abokan zama don samun wanzuwar zaman lafiya a kasa ba ki daya.
Advertisements
