News
Muhimman Bayanai Daga Cikin Jawabin Ranar Samun Yancin Kai Na Shugaba Tinubu
Muhimman Bayanai 13 Daga Cikin Jawabin Ranar Samun Yancin Kai Na Shugaba Tinubu
1. “Saboda sauye-sauyen da aka yi, kasarmu ta samu masu zuba hannun jari daga kasashen waje, wanda ya kai sama da dala biliyan 30.”
2. “Mun gaji sama da dala biliyan $33 cikin watanni 16.
3. “Mun biya bashin dala biliyan 7 da aka gada
4. “Mun share hanyoyin da ake bi bashi na sama da Naira tiriliyan 30
5. “Mun rage yawan bashi kaso 97% zuwa 68%”
6. “Mun yi nasarar ajiye rar kudi da ya kai Dala biliyan $37
7. “Mun samu nasarar kawar da mayakan Boko Haram sama da 300 a cikin shekara guda.”
8. “Mun amince da Asusun Ba daAgajin Bala’i don tara kudade masu zaman kansu da na jama’a don taimakawa alummar Najeriya cikin gaggawa
9. Gwamnatin Shugaba Tinubu ta ba da umarnin a gudanar da gwajin gaskiya a duk madatsun ruwa na kasar nan domin kaucewa bala’i a nan gaba.
10. Gwamnatin tarayya a shirye take ta taimakawa jahohi talatin da shida da har da Abuja FCT wajen siyan motocin CNG don zirga zirgar jama’a cikin rahusa.
11. “Mun yi farin ciki da aiwatar da Asusun Lamuni na Ilimin Najeriya (NELFUND)”
12. Nan ba da jimawa ba gwamnati za ta bayyana duk wadanda suka ci gajiyar karramawar kasa a 2024
13. Gwamnati za ta kira taron matasa na kasa na tsawon kwanaki 30 don magance batutuwan da suka shafi ilimi, aikin yi, da tsaro.
