Connect with us

Politics

ZABEN KANANAN HUKUMONI: Jam’iyyar APP Ta Lashe Kujeru 22 Cikin 23 A Ribas

Published

on

ZABEN KANANAN HUKUMONI Jam’iyyar APP Ta Lashe Kujeru 22 Cikin 23 A Ribas.
Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Jam’iyyar Action People’s Party (APP) ta lashe kujeru 22 daga cikin 23 a zaben kananan hukumomi da aka kammala a jihar Ribas.

Babban Jami’in Zabe na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Ribas (RSIEC) Adolphus Enebeli ya bayyana sakamakon zaben a Yau ranar Asabar a Fatakwal.

Advertisement

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Biyan Alawus Ga Rashin Yanayi Mai Kyau A Makarantu Da Kuma Ƙarancin Albashi

Sai dai alkalan zaben jihar sun dakatar da bayyana sakamakon karamar hukumar Etche (LGA) saboda ana ci gaba da tattara sakamakon zaben.

Enebeli ya ce za a bayyana sakamakon karamar hukumar Etche tare da na kujerun kansiloli 319 a nan gaba.

Idan ba’a manta gwamna Fubura na Jihar ta Ribas shine ya bayar Da Umarni Ga ‘yan Takarar Kananan Hukumomin Domin tsayawa Takara a Jam’iyyar APP Bayan Da tsohon gwamnan Jihar Nyesom Wike ya kwace Ragamar Jam’iyyar PDP a kotu.

Advertisement

Sai gwamna Fubura ya Yi zargin Rundunar Yan Sandan Nageriya Da Anfani Da bakin wuta Domin taimakawa PDP tsagin Wike.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *