Connect with us

News

Shugaban Tinubu Ya Naɗa Olufemi Olatubosun A Matsayain Sabon Shugaban Sojin Kasar Nageriya

Published

on

FB IMG 1730317548879
Spread the love

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

Advertisement

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa Manjo Janar Olufemi Olatubosun Oluyede a matsayin muƙaddashin babban hafsan sojin ƙasa.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya ce Olufemi zai ci gaba da riƙe muƙamin har lokacin da Janar Taoreed Lagbaja zai dawo ƙasar.

Advertisement

Kafin naɗa shi a muƙamin mukaddashin sojan Kasa Oluyede shi ne kwamandan runduna ta 56 da ke aiki a Jaji a jihar Kaduna.

Tun a makon da ya gabata rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa Janar Lagbaja yana jinya a wani asibiti a ƙasar waje bayan ta musanta rahotonnin da ke cewa ya rasu, tana mai cewa Manjo Janar Abdulsalami Ibrahim ne ya maye gurbinsa a matakin riƙon ƙwarya.

Daga baya hedikwatar tsaro ta Najeriya ta musanta batun, inda ta ce “babu wani batun muƙaddashin babban hafsan sojin ƙasa” a tsarin aikinta.

Advertisement

Manjo Janar Olufemi Olatubosun Yanada Shekaru 56 Kuma kafin nadashi a mukaddashin sojan Kasa na Nageriya ya rike mukamai da dama sannan Yanada Ya’ya uku da mata.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *