News
ASUU Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) reshen jami’ar jihar Bauchi, Sa’adu Zungur Unviersity (SAZU), sun sanar da shiga yajin aiki a kan rashin tsarin biyan kudin fansho da rashin biyansu wasu hakkokinsu na alawus.
Har ila yau, kungiyar ta ASUU ta bayyana cewa babu wani tanadi mai kyau na yin aiki da aka samar ga ma’aikatan jami’ar.
Jami’an Hukumar DSS Sun Saki Dan Fafutukar Kare Dimokradiyya Zubair A. Zubair
Shugaban kungiyar ASUU a SAZU, Kwamred Auwal Nuhu, shine ya sanar da tsunduma yajin aikin yayin wani taro da manema labarai da ya gudana ranar Juma’a a harabar jami’ar da ke Yuli.
Kwamred Auwal ya umarci mambobin kungiyar ASUU na SAZU da su shiga yajin aikin wanda ya fara daga misalin karfe 12:00 na ranar Juma’a, 29 ga watan Nuwamba, 2024.
“Kungiya ta gamsu cewa akwai sakaci da nuna halin ko in kula daga bangaren shugabancin jami’a da kuma bangaren gwamnati wajen biyan bukatun mu,” a cewar Kwamred Auwal.
Sannan, ya kara da cewa dukkan wani yunkurin kungiyar ASUU na ganin cewa hukumomi sun duba wadannan bukatu domin a warware matsalolin ya ci tura.
“A saboda haka, uwar kungiya ta amince mana cewa za mu iya shiga gagarumin yajin aiki na sai baba-ta-gani,” kamar yadda Kwamred Auwal ya bayyana.
Ya bayyana yanayin aiki a SAZU a matsayin ‘marar dadi’ tare da dora laifin a kan shugabancin jami’ar wanda ya gaza shawo kan matsalar duk da kiraye-kiraye da kungiyar ASUU ta dade ta na yi domin su dauki mataki.
“Ba zai yiwu mu cigaba da aiki a karkashin irin wannan yanayin ba. An tagayyara mambobinmu ta hanyar barinsu babu wani tsaro ta fuskar kudin shiga bayan shafe gomman shekaru su na aiki a jami’ar.
“Wannan yajin aikin shine mataki na karshe da kungiyar mu ta dauka bayan mun shafe tsawon shekaru ana tattaunawa ba tare da daukan wani mataki ba”, a cewar shugaban na ASUU a SAZU.a
Kwamred Auwal ya bayyana cewa yajin aikin ba zai kare ba har sai an dauki matakan zahiri domin kawo karshen matsalolin da ke damunsu.
WikkiTimes ta tattaro cewa yajin aikin zai kawo tsaiko a harkokin koyo da koyarwa sannan zai shafi alakar da ke tsakanin mahukunta da ma’aikatan jami’ar.
A duk lokacin da kungiyar ASUU ta shiga yajin aiki, dalibai su kan shiga halin kunci da damuwa saboda tsayawar karatunsu wanda kuma kai tsaye ya shaficigaban rayuwarsu.
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
