News
Innalillahi Wainnailaihi Rojiun : Allah Ya Yi Wa Mahaifin Nusaiba Abdullahi Tukuntawa Rasuwa
Innalillahi Wainnailaihi Rojiun : Allah Ya Yi Wa Mahaifin Nusaiba Abdullahi Tukuntawa Rasuwa
Cikin alhini da jimami, muke sanar da Al’umma rasuwar Mahaifin Nusaiba Abdullahi Tukuntawa,
Wannan labari mai girma ya girgiza iyalansa, da abokanan Iyalansa da dubban masoyata dake fadin jihar Kano .
Za a gudanar da jana’izar sa da misalin ƙarfe 8:00 na safe, a gidansu da ke unguwar Tukuntawa, cikin birnin Kano,
Jaridar INDA RANKA ta bayyana ta’aziyyarta ga iyalan marigayi Abdullahi tare da fatan Allah ya gafarta masa kuma ya bai wa iyalansa da masoyansa haƙuri da juriyar wannan babban rashi.
Nusaiba Abdullahi Tukuntawa ta kasance fitacciyar ma’aikaciya wadda ta bayar da gudunmawa wajen cigaban Jaridar INDA RANKA musamman wajen gudanar da shirye-shiryen da ke jan hankalin al’umma.
Allah ya jikan sa
