Connect with us

News

Yan Daba Sun Kashe Abokin Ango A Taron Ɗaurin Aure

Published

on

Dole Kowacce Gawa Ta Biya HarajiGwamnati

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI 

’Yan daba sun kashe wani ɗan shekara 25 a wurin taron ɗaurin auren babban abokinsa a Jihar Neja.

Advertisement

Matashin, mai suna Murtala Hassan, wanda shi ne babban abokin ango ya gamu da ajalinsa ne a yayin da yake rabon faɗa a wurin bikin auren a unguwar Barkin-Sale da ke garin Minna.

Mun Kama Masu Kwacen Wayoyi 1372, Da Masu Fadan Daba Sama Da 3000 — Anti Snatching Force 

Shaidu sun ce matashin wanda ke sana’ar ɗinki ya rasu ne bayan an soka masa wuƙa a rikicin ƙungiyoyin ’yan daba masu gaba da juna ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na dare.

Advertisement

 

Wani mazaunin unguwar Barikin-Sale ya ce, rikicin kungiyoyin an daɗe ana yin sa, ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.

Advertisement

Kakakin ’yan sanda a Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin da cewa sun samu rahoton kashe matashin a lokacin da yake ƙoƙarin raba faɗan ɓata-gari.

Ya ce ’yan sanda sun je sun ɗauke gawar a wurin inda suka kama mutum guda da ake zargi, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar lamarin kamar yanda Jaridar AMINIYA ta ruwaito

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending