News
Bana Yin Shiri Da Shugaba Tinubu Saboda Yana Kawo Manufofin Da Suke Cutar Da Talakawa — Gwamnan Bauchi
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad, yace ba yayin shiri da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, saboda yana kawo manufofin da suke cutar da talakawan Najeriya.
Bala Mohammed Kauran Bauchi ya fa’dawa Sheikh Jingir hakan a lokacin wata Ziyara da shehun malamin ya Kai wa Gwamnan a gidan Gwamnatin Jihar dake Bauchi.
Sabon Mai Baiwa Gwamnan Kano Ya Rasu Kwana Daya Bayan Rantsar Da Shi
A Cikin wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumuntar zamani an Hango Gwamna Yana magana kan masu Muslim-Muslim Ticket tare da Halin da Gwamnatin ta jefa al’ummar Najeriya .
Bisa wasu kudure da Shugaban kasar ya gabatar musamman kudrin dokar sake Fasalin Harajin Wanda Gwamnan Yace Babu abinda dokar Zata haifar face cutar da Arewacin Nageriya .
Hakan yasa bana shiri da Shugaban kasa domin ya kawo tsarin da zai cutar da al’ummar Arewacin Nageriya inji Gwamna yake fadawa Sheikh sani Yahaya Jingir.
