Connect with us

News

Babbar Magana: An Kama Lauyan Bogi Ana Tsaka Da Shari’a A Kotu

Published

on

An kama lauyan bogi ana tsaka da shari'a a kotu

DAGA MAIMUNA RABIU UMAR 

Rundunar ƴansanda ta kama wani da ake zargin lauya na bogi ne mai suna Godwin Eguabor yayin da ya ke wakiltar wani mutum a wata kotu da ke jihar Legas.

Advertisement

Rahotanni na nuni da cewa Eguabor ya bayyana a gaban wata kotun majistare da ke yankin Badagry a Legas a ranar Laraba a matsayin lauya da ke wakiltar wani mai kara.

Wata Budurwa Ta Rasu Sanadiyyar  Gobara Da Ta Kama Cikin Gidan Su A Kano

Atule Elchors, mataimakin shugaban kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Badagry, ya ce yayin zaman kotun a ranar Laraba, Eguabor ya bayyana kansa a matsayin lauya da ke wakiltar wani.

Advertisement

Elchors ya bayyana cewa ya dade yana jin jita-jitar wani lauya na bogi na gudanar da ayyukan lauya a yankin Badagry.

“Mun tambaye shi lambar kotun koli, wadda ita ce lambar rajista ta kowanne lauya, amma bai iya bayar da amsa ba, sai dai labaru marasa tushe ya ke ba mu.

Advertisement

“Abin takaici ma shi ne sunan da ya ke amfani da shi a kotu ya bambanta da sunan da ya ba wa ƴansanda lokacin da su ka kama shi.”

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending