News
Lauya Ya Maka Alƙali A Babbar Kotun Tarayya Bisa Zargin Cin Zarafi
A wani lamari da ba kasafai ake samu ba, wani lauya mai zaman kansa, Barista Isa Hassan Na Laraba, ya maka wani alƙali a gaban Babbar Kotun Tarayya bisa zargin cin zarafi.
Babbar Kotun Tarayya da ke Lafia, babban birnin Jihar Nasarawa, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Justine Olajunwon, ta fara sauraron karar da Barista Isa Hassan Na Laraba ya shigar. Lauyan ya shigar da ƙara ne kan Mai Shari’a Abdullahi Hassan Shams Shama, wanda ke shari’a a Babbar Kotun Doma, yana zarginsa da cin zarafi.
Wannan shari’a ta ja hankalin al’umma, kasancewar ba kasafai ake samun irin wannan ƙara daga lauya zuwa alƙali ba. Ana sa ran shari’ar za ta ci gaba da gudana yayin da kotu ke tantance hujjoji daga ɓangarorin da suka shigar da ƙara da kuma waɗanda ake ƙara.
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
