News
An Kullewa Gwamna Fubara shiga Kofar Majalisar Dokokin Ribas
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rahotanni sun bayyana cewa Majalisar Dokokin Jihar Ribas ta hana Gwamna Similanayi Fubara shiga cikinta a safiyar wannan Larabar.
Aminiya ta rawaito gwamnan ya ziyarci majalisar da ke yankin Aba na birnin Fatakwal ne domin gabatar mata da Kasafin Kuɗin jihar na 2025.
Sai dai isowar gwamnan tare da tawagarsa, ya tarar da ƙofar shiga majalisar a garƙame da kwaɗo kuma an ƙi buɗewa da ke tabbatar da alamar ba a maraba da zuwan nashi.
Babu wani ƙwaƙwaran dalili da aka bayar, sai dai bayanai sun rawaito cewa an rufe wa gwamnan ƙofa ne saboda bai sanar da majalisar a hukumance cewa zai zo gabatar da Kasafin Kuɗin jihar ba.
Advertisements
