Connect with us

News

Gwamnatin Kano Za Ta Ginawa Masu Lalurar Laka Cibiyar Fasahar Sadarwa Domin Inganta Rayuwarsu

Published

on

IMG 20250130 WA0029

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada Kudirinta na tallafawa masu bukata ta musamman, musamman masu lalurar laka domin inganta rayuwarsu.

Advertisement

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan yayin rabon kayan tallafi da kungiyar masu fama da lalurar laka ta baiwa ya’yan kungiyar da hadin gwiwar gidauniyar MacArthur.

Wani Mahaifi Ya Harbe Yar’sa  Sakamakon Yada Bidiyoyinta A Tiktok 

Kwamishina Waiya ya ce yana da muhimmanci a tallafawa masu fama da lalurar laka saboda mawuyacin halin da suke ciki sakamakon lalurar da kuma iyalansu.

Advertisement

Ya ba su tabbacin gwamnatin jihar Kano za ta cigaba da fito da tallafin don ingantawa masu lalurar.

Kwamishinan ya ce gwamnatin Kano za ta hada hannu da kungiyar domin samar da cibiyar fasahar sanarwa, sannan a sanya musu kayan aikin a koya musu don inganta rayuwarsu.

Advertisement

A wata sanarwa da daraktan aiyuka na musamman na ma’aikatar yada labarai Sani Abba Yola ya aikowa Kadaura24, ya ce Waiya ya yabawa iyalan wasu lalurar saboda yadda suke tallafawa yan uwansu, sannan ya ba su tabbacin gwamnatin jihar Kano zata cigaba da tallafawa musu don saukaka musu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending