News
ZAZZABIN LASSA: Mutum 214 sun kamu, 39 sun rasu a cikin makonni uku a Najeriya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Mutum 214 sun kamu sannan wasu mutum 39 sun mutu a jihohi 10 daga ranar 30 ga Disembar 2024 zuwa ranar 19 ga Janairu.
Bisa ga rahoton da hukumar NCDC ta fitar ranar Alhamis ya nuna cewa an gano haka ne a kananan hukumomi 43 a kasar nan.
Hukumar ta ce a tsakanin wannan lokacin an samu mutum 843 da ake zargin sun kamu da cutar.
Jihohin da cutar ta bullo sun hada Ondo -82, Edo-47, Bauchi -35, Taraba -31, Ebonyi -6, Gombe-4, Kogi-4, Filato-3, Delta-1 da Nasarawa -1.
Mutanen da suka mutu an gano su a jihohin Ondo-8, Edo-9, Bauchi-4, Taraba-9, Ebonyi-3, Gombe-3, Kogi-1, Filato-1 da Nasarawa -1.
Hukumar ta ce an samu ragi a yawan mutanen dake kamuwa da cutar daga mutum 89 zuwa mutum 71.
An gano kashi 77% na mutanen da suka kamu da cutar a jihohin Ondo, Edo da Bauchi.
NCDC ta ce za ta ci gaba da kokari wajen ganin ta dakile yaduwar cutar a kasar nan.
