Connect with us

News

ZAZZABIN LASSA: Mutum 214 sun kamu, 39 sun rasu a cikin makonni uku a Najeriya

Published

on

LASSA FEVER PIX

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Mutum 214 sun kamu sannan wasu mutum 39 sun mutu a jihohi 10 daga ranar 30 ga Disembar 2024 zuwa ranar 19 ga Janairu.

Advertisement

Bisa ga rahoton da hukumar NCDC ta fitar ranar Alhamis ya nuna cewa an gano haka ne a kananan hukumomi 43 a kasar nan.

Yan hidimar ƙasa za su fara karɓar sabon alawus na Naira dubu 77 a watan Fabrairu mai kamawa —Shugaban NYSC

Hukumar ta ce a tsakanin wannan lokacin an samu mutum 843 da ake zargin sun kamu da cutar.

Advertisement

Jihohin da cutar ta bullo sun hada Ondo -82, Edo-47, Bauchi -35, Taraba -31, Ebonyi -6, Gombe-4, Kogi-4, Filato-3, Delta-1 da Nasarawa -1.

Mutanen da suka mutu an gano su a jihohin Ondo-8, Edo-9, Bauchi-4, Taraba-9, Ebonyi-3, Gombe-3, Kogi-1, Filato-1 da Nasarawa -1.

Advertisement

Hukumar ta ce an samu ragi a yawan mutanen dake kamuwa da cutar daga mutum 89 zuwa mutum 71.

An gano kashi 77% na mutanen da suka kamu da cutar a jihohin Ondo, Edo da Bauchi.

Advertisement

NCDC ta ce za ta ci gaba da kokari wajen ganin ta dakile yaduwar cutar a kasar nan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending