Connect with us

Uncategorized

Yan hidimar ƙasa za su fara karɓar sabon alawus na Naira dubu 77 a watan Fabrairu mai kamawa —Shugaban NYSC

Published

on

NYSC Members 700x430

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Advertisements
Advertisements

Darakta Janar na Hukumar kula da Ƴan Hidimar Kasa (NYSC), Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya bayyana cewa za a fara biyan ‘yan hidimar ƙasa sabon tsarin alawus na Naira dubu 77 a kowane wata daga watan Fabrairun 2025.

Advertisements

Da ya ke jawabi a jiya Alhamis ga ‘yan hidimar kasa na rukunin ‘C’ II na 2024 a Katsina, Ahmed ya tabbatar da cewa tuni an saka karin alawus din a kasafin kudin gwamnatin tarayya na 2025 kuma zai fara aiki da zarar an amince da shi.

Advertisements
Advertisements

Ma’aji Ya Nuna Bacin Rai Kan Aikin Makaranta a Doguwa, Ya Bada Sammacin Dan Kwangilar

“Wannan watan (Janairu) ya riga ya kare, amma da zarar an amince da kasafin kudi, nan da watan gobe (Fabrairu), za a fara biyan ku N77,000 maimakon N33,000 da aka saba biya,” in ji shi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending