News
Wani Magidanci Ya Guntule Wa Matarsa Hannu Da Adda Bisa Zarginta Da Aikata Zina
DAGA KABIR BASIRU FULATAN
Rundunar Ƴan sandan jihar Enugu ta tabbatar da kama wani magidanci mai suna Sunday Echege da laifin guntile hannun matarsa
Magidancin mai kimanin shekaru 33 ya yanke hannun hagun matar tasa mai suna Chinonso Echege da adda bisa zarginta da ya’yi da aikata zina.
Kakakin rundunar Yan Sanda Jihar Enugu Daniel Ndukwe shine ya sanar da haka a wata takarda daya fitar ga manema labarai a makon Jiya.
ya ce Echege ya aikata hakan a cikin gidansa dake kauyen Ibagwa-Agu a karamar hukumar Nsukka.
Sai dai kakakin rundunar Yan sandan Ndukwe bai fadi Ranar da abin ya faru amma Ya ce Jamia’ansu dake karkashin rundunar Okpuje ne suka kama magidancin ranar Lahadin makon jiya.
Kakakin ya ce jami’an tsaron sun kama Echege ɗauke da addan da ya guntile hannun matarsa da shi.
Ya ce Echege na tsare a ofishinsu kuma idan sun kammala bincike za su kai magidancin kotu domin yanke masa hukunci.
