Connect with us

News

A Yi Siyasa Cikin Mutunci Da Girmamawa – Waiya Ga ‘Yan Adawa

Published

on

IMG 20250211 WA0015

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya yi kira ga masu magana a gidajen rediyo, musamman ‘yan jam’iyyun adawa, da su rika yin adawa mai ma’ana cikin mutunci da girmamawa.

Advertisement

Waiya ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da masu magana a gidajen rediyo, ciki har da wakilai daga jam’iyyun siyasa daban-daban. Ya jinjinawa halartar su, yana mai cewa hakan ya nuna kishinsu ga jihar Kano, domin da ba sa kishin Kano, ba za su halarci taron ba.

Marken Mahuta: Kauyen Da Kalubalen Ilimi Da Rashin Lafiya Suka Addaba A Kano 

A yayin jawabin nasa, ya jaddada mahimmancin adawar siyasa ta hanyar kaucewa kalaman da ba su dace ba. Ya ce duk da bambance-bambancen jam’iyya, wajibi ne a mutunta juna don inganta siyasa mai tsafta.

Advertisement

A wani bangare na kokarinsa na kyautata harkokin siyasa a Kano, kwamishinan ya sake nanata shirin farfado da kungiyar Gauta Club, wacce a baya ta taka muhimmiyar rawa wajen hada kan masu magana a gidajen rediyo ba tare da la’akari da bambancin jam’iyya ko ra’ayi ba.

Shugaban kungiyar Gauta a Kano, Alhaji Hamisu Danwawu Fagge, ya yabawa Kwamishinan bisa wannan kokari, yana mai cewa shirin zai taimaka wajen tsaftace harkar magana a kafafen yada labarai da kuma ci gaban Kano gaba daya.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending