Connect with us

News

An Gurfanar Da Matasa Biyu A Kotu Bisa Zargin Satar Leda

Published

on

An kama lauyan bogi ana tsaka da shari'a a kotu
Advertisements
ads

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

An gurfanar da wasu matasa biyu, Habeeb Akinbolu mai shekaru 40 da Daniel Akinola mai shekaru 45 a gaban kotun majistare da ke Ota, Jihar Ogun, bisa zargin satar bandir din leda wanda kudinsa ya kai N30,000 mallakar mai gidansu.

Ana tuhumar wadanda ake zargin, waɗanda ba a bayyana adireshinsu ba, da laifuffukan hada kai da sata.

Hukumar Yaki da Rashawa Ta Kama Jami’an Karamar Hukumar Nasarawa da Hadimin Gwamna Bisa Zargin Karkatar da Naira Miliyan 105

Mai gabatar da kara, Insp. E.O. Adaraloye, ya bayyana wa kotu cewa wadanda ake zargin sun aikata laifin ne a ranar 10 ga Janairu, da misalin karfe 7 na yamma, a kamfanin Mercury dake kan babbar hanyar Lagos zuwa Abeokuta, Ota.

Adaraloye ya ce waɗanda ake zargin, wadanda ke aiki a kamfanin Mercury Mill, an kama su ne a wurin tsaro na ƙofar shiga kamfanin dauke da fakitin Ledar.

An dage sauraron karar zuwa ranar 4 ga Maris, domin ci gaba da shari’ar.

Advertisement

 

 

DAILY NIGERIAN 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending