Connect with us

News

Sanata Natasha Ta Kai Karar Akpabio Zuwa Majalisar Duniya Ta Kungiyar Majalisun Duniya (IPU)

Published

on

Natasha Women in parliament 750x430

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, da aka dakatar daga Majalisar Dattawan Najeriya, ta daukaka karar dakatarwarta zuwa Kungiyar Majalisun Duniya (IPU) a Majalisar Dinkin Duniya (UN) da ke birnin New York.

Sanatar daga Jihar Kogi, wadda Majalisar Dattawa ta dakatar makon jiya bisa zargin karya dokokinta, ta nemi adalci daga kungiyoyin kasa da kasa da ke kare dimokuradiyya.

Advertisement

Haƙƙin Gyaran Arewa Ba Wai Aikin Shugabanni Ne Kawai Ba Aikin Kowa Ne

A yayin zaman IPU, ta bayyana dakatar da ita a matsayin “ba bisa ka’ida ba,” tana mai cewa an tauye hakkinta na dimokuradiyya.

Bayan jawabinta, Sanata Natasha ta nuna damuwa kan tsaron lafiyarta, tana zargin cewa wasu manyan jiga-jigan siyasa a Najeriya na iya hana ta dawowa daga New York saboda matakin da ta dauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending