Connect with us

News

Shugaba Tinubu ya dakatar da gwamnan Rivers da mataimakin sa da yan majalisar jihar na watanni 6.

Published

on

Siminalaye Fubara 750x430

 

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara, da mataimakiyar sa Mrs. Ngozi Odu, har na tsawon watanni 6.

Advertisement

Shugaba Tinubu ya bayyana daukar matakin ne a cikin wani takaitaccen jawabin sa da ya gabatar a cikin daren Talatar nan, ya ce ya yi amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi wajen sanya wannan doka wacce ta kwace mulkin jihar daga hannun gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakin sa har sai lamura sun dawo dai-dai a jihar.

Kazalika, shugaba Tinubu ya kuma bayyana dakatar da dukkanin yan majalisar dokokin jihar suma na tsawon watanni shidan.

Advertisement

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan rikicin siyasar da ya dade da kunno kai a tsakanin gwamna Fubara da ministan birnin tarayya Abuja Nyesome Wike, al’amarin da ya janyo takun saka tsakanin sa da yan majalisar dokokin jihar.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending