Connect with us

News

Gwamnatin Kebbi Ta Musanta Rufe Jami’ar Aliero Saboda Cutar Sankarau

Published

on

Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Musanta Rufe Jami'ar Aliero Saboda Cutar Sankarau

 

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata jita-jitar da ke yawo cewa ta rufe Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliero sakamakon bullar cutar sankarau, wacce ta yi sanadin mutuwar akalla dalibai 11.

Advertisement

Sai dai gwamnatin ta tabbatar da ɓullar cutar a jami’ar, amma ta ce tuni ta ɗauki matakan dakile yaduwarta.

Mata Da Ke Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga Ta Shiga Komar ‘Yan Sanda

Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi na Jihar Kebbi, Alhaji Isa Abubakar Tugga, ya tabbatar da hakan, yana mai jaddada cewa babu wata umarni daga gwamnati na rufe jami’ar.

Advertisement

Tun jiya Laraba ne dai rahotanni suka cika shafukan sada zumunta da ke cewa an rufe jami’ar saboda cutar sankarau, lamarin da gwamnatin ta ce ba shi da tushe.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending