Connect with us

News

Kotu Ta Bada Damar Yin Kiranye Ga Sanata Natasha

Published

on

FB IMG 1741274096504

Babbar Kotun Tarayya dake Lokoja, Jihar Kogi, ta yanke hukuncin cewa Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) na da damar karɓar bukatar yin kiranye da al’ummar mazaɓar Kogi ta Tsakiya suka gabatar akan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

A hukuncin da aka yanke a ranar Juma’a, kotun ta tabbatar da cewa yin kiranye abu ne da doka ta amince da shi, don haka al’umma na da ‘yancin aiwatar da bukatarsu cikin lumana da bin doka.

Advertisement

Gobara Ta Tashi a Gidan Mai A Neja Bayan Fashewar Tanka

Kotun ta kuma yi gargadi ga INEC da jami’anta kan karɓar korafe-korafen da ke dauke da sanya hannu na bogi ko kuma yin hukunci a kansu ba tare da bin ka’idar doka ba.

An dage sauraron ƙarar zuwa ranar 6 ga watan Mayu, 2025, inda za a ci gaba da tantance sahihancin bukatar kiranyen.

Advertisement

 

 

Advertisement

CHANNELS TV

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending