News
Masu Haƙar Kaburbura Sun Koka Kan Ƙarancin Alawus Da Matsalolin Maƙabarta A Kano
Masu haƙa kaburbura da gyara maƙabarta a Kano sun koka kan ƙarancin alawus ɗin da ake ba su, wanda ya ragu daga N5,000 zuwa N3,000 ko ma ƙasa da haka a wasu lokuta.
Malam Suleiman Mohammed, wani mai haƙar kabari a maƙabartar Tudun Wada, ya bayyana cewa a wasu lokutan ana shafe watanni ba tare da an biya su ba. Ya ce sun kai ƙorafinsu gaban Sarkin Kano, inda aka yi musu alƙawarin duba lamarin.
Masu Tauna Cingam Na Haɗiye Ƙananan Robobi Ba Tare Da Sun Sani Ba – Masana
A cewarsa, aikin haƙa kabari yana da hatsari kuma yana da buƙatar ƙarfi, don haka yana da kyau a inganta alawus ɗinsu. Bugu da ƙari, ya koka kan yadda ɓata gari ke amfani da maƙabarta wajen shaye-shaye da adana makamai kamar yanda ya shidawa BBC
Ya nemi a inganta ayyukansu ta hanyar tsaftace maƙabartar da gyara katangarta da sanya fitulu.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
