Connect with us

News

MURNAR SALLAH: Mu Ci Gaba Da Rayuwa Cikin Zaman Lafiya Da Soyayya – Amb. Bello Sani Maitakalma

Published

on

IMG 20250330 WA0026

A yayin da al’ummar Musulmi ke gudanar da bukukuwan karamar Sallah a fadin duniya, Amb. Bello Sani Maitakalma, Sa’in Hausawan Afrika, Jarumin Arewa, Garkuwar Sarkin Malaman Abuja, kuma Shugaban rukunin kamfanin Maitakalma Global Travels, ya taya al’ummar jihar Kano da Arewacin Najeriya baki daya murnar Sallah.

Ya jaddada muhimmancin darusan watan Ramadan, musamman hakuri, yafiya, jin kai da taimakon juna, yana mai kira ga Musulmi da su ci gaba da rayuwa bisa wadannan kyawawan dabi’u.

Advertisement

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Sallah

Amb. Bello Sani Maitakalma ya bukaci matasa da su kasance masu kishin zaman lafiya, su guji duk wani abu da zai kawo tashin hankali ko rarrabuwar kawuna a cikin al’umma.

Haka nan, ya yi fatan alheri ga kowa tare da addu’ar Allah ya karbi ibadun da aka gudanar a Ramadan, ya ba da lafiya, zaman lafiya, da ci gaban tattalin arziki a Najeriya.

Advertisement

Amin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending