News
‘Yan Sanda Sun Gayyaci Sarki Sunusi Kan Rikicin Da Aka Samu A Tawagarsa A Ranar Sallah
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta gayyaci Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, domin amsa tambayoyi kan rikicin da ya auku yayin hawan Sallah da ya gudana karkashin kulawarsa, wanda ya haifar da mutuwar wani matashi.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan sashin bayanan sirri, Olajide Rufus Ibitoye, ya sanya wa hannu, rundunar ta bayyana cewa gayyatar na da nufin gudanar da cikakken bincike kan yadda lamarin ya faru da kuma gano hakikanin musabbabin rikicin.
Bashin Najeriya Ya Kai Naira Tiriliyan N144.67 A 2024 – Rahoton DMO
Sanarwar ta bukaci Sarkin da ya bayyana a shelkwatar ‘yan sanda da ke Abuja a ranar Talata, 8 ga Afrilu, 2025 da misalin karfe 10:00 na safe. An bayyana cewa umarnin gayyatar ya fito ne daga Babban Sufeton ‘yan sanda na kasa, Kayode Egbetokun, domin tabbatar da gaskiya da adalci game da lamarin da ya girgiza al’ummar Kano.
Rundunar ‘yan sanda ta ce wannan mataki na daga cikin kokarinta na tabbatar da doka da oda, tare da tabbatar da cewa kowane dan kasa yana da alhakin bayyana bayani idan bukatar hakan ta taso, ba tare da la’akari da matsayinsa a al’umma ba.
Lamarin rikicin da ya auku cikin tagawar sarkin yayin hawan Sallah ya janyo cece-kuce a fadin kasar, inda aka ruwaito mutuwar wani matashi. Wannan ya kara jaddada bukatar gudanar da bincike mai zurfi domin gano gaskiyar lamarin.
Rundunar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankula tare da bai wa hukumomi hadin kai wajen tabbatar da gaskiya da adalci.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
