News
Mata Biyu Sun Rasa Rayukansu Sakamakon Faɗawa Kudiddifi A Kano
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wasu mata biyu sakamakon faɗawa cikin wani ramin kudiddifi da ke ƙaramar hukumar Gezawa a jihar.
Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aike wa jaridar Inda Ranka a daren Talata. Ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a safiyar ranar Talata, yayin da aka samu kiran gaggawa daga shugaban jami’an sintiri na karamar hukumar Gezawa.
SATAR KAYAN MAKARANTU: Hukumar NSCDC Ta Kama Mutane Biyar A Kano
A cewarsa: “Da misalin ƙarfe 11:15 na safiyar jiya ne muka samu kiran neman agaji, inda aka bayyana mana cewa wasu mata biyu sun faɗa cikin kudiddifi tun daren Litinin. Nan take muka tura jami’anmu domin gudanar da aikin ceto.”
Bayan isar jami’an hukumar, an samu nasarar ciro matan daga cikin ramin, sai dai likitoci sun tabbatar da mutuwarsu. Daga nan aka mika gawarwakin ga jami’in ‘yan sanda na Caji Ofis ɗin Gezawa, Musa Garba, domin ci gaba da bincike da kuma daukar matakan doka.
Sanarwar ta ƙara da bayyana cewa matan sun faɗa cikin kudiddifin ne a yayin da suka je su ɗauraye jikinsu, bayan sun kammala aiki a wani kamfanin sarrafa zoɓo da ke yankin.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
