Connect with us

News

Kyari Ya Ce Ba Ya Hannun EFCC

Published

on

images (5)

Tsohon Shugaban Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL), Engr. Mele Kyari, ya ce ba gaskiya ba ne rade-radin da ke yawo cewa Hukumar EFCC ta kama shi ko tana tsare da shi.

Kyari ya bayyana hakan ne a wata wallafa da ya yi a shafinsa na X a daren Asabar, 3 ga watan Mayu, yana mai cewa yana rayuwa cikin gaskiya da tsoron Allah tun lokacin da ya fara aiki a NNPC fiye da shekaru 30 da suka wuce.

Advertisement

Yadda Aka Buɗe Makarantar Koyon Wanki Da Guga A Asibitin AKTH 

“Ban yi wa Najeriya kadai aiki ba, na yi da tsoron Allah,” in ji shi cikin martaninsa ga rade-radin da ke yawo.

A baya dai rahotanni sun bayyana cewa Hukumar EFCC ta fara binciken wasu tsofaffin jami’an NNPCL, musamman wadanda suka rike mukamai a matakin gudanarwa da kuma matatun man Warri, Kaduna da Fatakwal.

Advertisement

Wata jaridar yanar gizo ce ta wallafa cewa an kama Kyari don amsa tambayoyi kan zarge-zargen almundahana, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Sai dai Kyari ya yi fatali da ikirarin, yana mai cewa ba ya cikin tsare, kuma bai da hannu a cikin duk wata almundahana da ake zargi da ita.

Advertisement

A kwanakin baya ne aka fara duba wasu kudade da suka hada da Dala biliyan 2.96 da ake zargin an karkatar, inda aka ruwaito cewa an gano Naira biliyan 80 a asusun wani tsohon darekta a kamfanin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending