Connect with us

News

Sojojin Najeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Dubu 13 Da 500 – Badaru Abubakar

Published

on

1746657332623

Ministan Tsaro na Tarayya, Mohammed Badaru Abubakar, ya ce dakarun Najeriya sun kashe fiye da ‘yan ta’adda 13,500 tun bayan hawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Badaru ya bayyana haka ne yayin da yake bayani kan nasarorin da gwamnatin ta samu a bangaren tsaro cikin shekara biyu da suka gabata.

Advertisement

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Kafafen Yaɗa Labarai Kan Tallata ’Yan Ta’adda

Ya ce gwamnatin Tinubu ta gaji matsanancin kalubale a fannin tsaro, amma yanzu abubuwa sun inganta sosai, musamman a yankin Arewa maso Gabas da wasu sassa na kasar.

A cewarsa, “A baya idan aka ce Gambaru ko Bama, mutane kan firgita saboda barazanar ‘yan ta’adda, amma yanzu komai ya canza. Haka nan hanyar Abuja zuwa Kaduna da ke fama da garkuwa da mutane yanzu ta dawo lafiya.”

Advertisement

Ministan ya ce tun daga watan Mayun 2023 zuwa yanzu, sojoji sun kashe ‘yan ta’adda sama da 13,500, inda kuma suka hallaka sama da shugabannin Boko Haram 300 a fadin Najeriya.

Ya kara da cewa a yankin Kudu maso Gabas, jami’an tsaro sun kama wata mota dauke da katan 18,000 na harsasai da fakiti 250 na wasu makamai masu hadari.

Advertisement

A bangaren kama masu aikata laifi, Badaru ya ce an cafke ‘yan ta’adda 17,469, tare da ceto mutane 9,821 da suka fada hannun miyagu. Haka kuma an gano wani wuri da ake kera bindigogi a Jihar Filato, inda aka lalata makamai da dama.

Ministan ya ce ficewar kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso daga ECOWAS ba ta shafi tsaron Najeriya ba, saboda matakan da gwamnati ta dauka na hadin gwiwa da jami’an tsaro a kan iyakokin kasar.

Advertisement

Ya  ce gwamnati na kokarin dakile yaduwar matsalar tsaro zuwa Kudu maso Yamma, ta hanyar dakatar da motsin ‘yan ta’adda daga yanki zuwa yanki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending