News
Yan Ta’adda Sun Kai Farmaki Masallatai Ana Tsaka Da Yin Sallar Juma’a A Katsina
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu yan ta’adda da ake kyautata zatun yan Bindiga ne dauke da muggan makamai sun kaiwa masu Sallar juma’a hari a garin Dan-Ali na karamar hukumar Dan musa dake jihar Katsina.
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa maharan sun kai farmaki masallatai masu yawa lokacin da mutane suke tsaka da yin Sallar juma’a.
Haka zalika yan ta’addan sun mamaye masallata tare da bude wuta akan mutanen garin , hakan tasa dole masu yin Sallar jumma a gudun neman tsira da rayuwar su
Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa mazauna garin sun ji harbin bindiga lokacin da suke yin Sallar jumma a, inda kowa ya gudu Kuma ba’a kai ga kammala Sallar ba.
Kawo lokacin rubuta Wannan labari ba’a samu damar jin ta bakin kakakin rundunar yan sandan jihar Katsina akan faruwar lamarin ba.
