News
Gwamnatin Kano Ta Ware Kuɗi Mai Yawa Don Gyara Gadan Bayan Gobarar Masallaci
Gwamnatin Jihar Kano ta ware kuɗi naira miliyan 151,863,895.97 domin gudanar da ayyukan more rayuwa a garin Gadan dake ƙaramar hukumar Gezawa.
Wannan na zuwa ne bayan gobarar da ta tashi a masallaci a garin a watan Mayun 2024, inda wasu mutane suka rasa rayukansu.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya sanar da wannan a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai.
‘Yan sanda Sun Tabbatar Da Rasuwar DPO A Rano, Sakamakon Hatsaniyar Da Ta Faru
A cewar sanarwar, kudin da aka ware zai taimaka wajen:
Gina sabon masallaci da zai maye gurbin wanda gobara ta lalata,
Gina ajujuwa biyu da ofishin malamai,
Gyaran bandakuna guda shida,
Samar da rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana, wacce za ta haɗa da babban tankin ruwa.
Gwamnatin jihar ta yi alkawarin ganin an kammala ayyukan cikin gaggawa don farfaɗo da rayuwar al’ummar yankin.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
