Connect with us

News

DA DUMI-DUMI: Gobara Ta Tashi A Wani Otel Na Alhazan Najeriya A Makkah

Published

on

1749305389891

Wata gobara ta tashi a wani otel da ke kan titin Shara Sittin a birnin Makkah, wanda ke dauke da wasu alhazan Najeriya da suka je aikin Hajji a bana.

Sai dai, cikin ikon Allah, ba a samu asarar rai ko guda ba, domin a lokacin da gobarar ta tashi, alhazan na cikin tantunansu da ke Mina, wajen garin Makkah.

Advertisement

Jam’iyyar PDP Ta Roƙi Peter Obi Ya Koma Cikinta

DCL HAUSA ta ruwaito cewa hukumar jin dadin alhazai ta Najeriya (NAHCON) sun tabbatar da aukuwar lamarin, tare da bayyana cewa tuni an dauki matakin gaggawa wajen samun mafita.

Wani jami’i daga NAHCON ya bayyana cewa alhazan da abin ya shafa – kimanin mutum 484 – galibinsu ‘yan International ne, wato wadanda suka biya kudin kujerarsu ta hannun kamfanonin yawon shakatawa masu zaman kansu.

Advertisement

Hukumomin Saudiyya sun iso wajen cikin gaggawa domin kashe wutar, kuma tuni NAHCON ta samar da wani otel na wucin gadi domin saukar da alhazan da abin ya shafa.

Za mu ci gaba da bibiyar wannan lamari, don kawo muku karin bayani.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending