Connect with us

News

Iran Ta Yi Ruwan Makamai Masu Linzami Kan Isra’ila

Published

on

34f04ab550d7f4d5c208b37e86502dd0c39794b42b26df6d4e9bf72e23f2b988
Yadda Iran ta zazzaga wa Isra'ila makamai masu linzami a birnin Haifa.
Spread the love

An wayi gari a ranar Litinin da cigaba da luguden wuta tsakanin kasashen Iran da Isra’ila, wanda ya barke tun ranar Juma’a bayan da Isra’ila ta kai hari kan Tehran.

Iran ta mayar da martani ta hanyar ruwan makamai masu linzami kan biranen Isra’ila da suka hada da birnin Haifa, inda cibiyar makamashi take.

Shugaba Tinubu Ya Ba Da Umarnin Gaggauta Dakile Rikicin Jihar Benue

A nata bangaren, Isra’ila ta tashi da jiragen yakin ta inda ta kai hare-hare a kan wasu wurare a kasar Iran ciki har da ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Advertisement

Rahotanni daga Isra’ila sun nuna cewa mutum hudu ne suka rasa rayukansu, tare da rushewar wasu gine-gine a birane daban-daban.

Iran ta bayyana cewa dakarun juyin juya halinta ne suka kaddamar da farmakin safiyar Litinin, inda ta ce an kai hare-haren ne a wurare na musamman.

Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa kasar sa ba ta da niyyar kera makaman nukiliya, kuma tana da ‘yancin ci gaba da amfani da makamashi na nukiliya don ci gaban tattalin arziki. Ya kara da cewa jagoran addinin kasar, Ayatollah Ali Khamenei, bai amince da sarrafa makaman kare dangi ba.

Advertisement

Rahotanni da suka zuwa yanzu sun bayyana cewa Iran ta rasa mutane 224 yayin da Isra’ila ta yi asarar mutane 18.

Wannan sabon rikici na kara jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin hali na fargaba da kuma kira daga kasashen duniya da su shiga tsakani don dakile barkewar yaki gaba daya.

 

Advertisement

 

DW

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *