News
Barau FC Ta Sauka Asaba Domin Fafatawa A Gasar NNL Super 8
Kungiyar kwallon kafa ta Barau FC da ke Kano ta isa birnin Asaba na jihar Delta domin shiga gasar NNL Super 8, wadda ke share fagen shiga gasar Firimiyar Najeriya (NPFL) ta kakar wasa ta 2025/2026.
Tawagar kungiyar wadda ake yi wa laƙabi da Maliya Boys ta sauka a Asaba ne a ranar Laraba, inda ta je da ‘yan wasa 32 tare da jami’ai da masu horarwa fiye da 15.
Gwamnatin Kano Ta Yabawa Gwamnatin Tarayya Bisa Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar NCC A Jihar
Jami’in yaɗa labarai na kungiyar, Ahmad Hamisu Gwale, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.
Barau FC na fatan samun tikitin shiga gasar Firimiyar Najeriya a karon farko tun kafuwarta, inda za ta fafata da sauran ƙungiyoyi guda bakwai da suka samu nasarar zuwa wannan mataki.
Gasar Super 8 za ta gudana daga 5 zuwa 12 ga watan Yuli, 2025 a filin wasa na Stephen Keshi da ke Asaba.
An raba ƙungiyoyin gasar gida biyu – Arewa da Kudu – inda daga kudu ake da Warri Wolves, Osun United, Crown FC, Kun Khalifa FC.
Daga Arewa kuwa akwai Wikki Tourists (Bauchi), Yobe Desert Stars, Doma United (Gombe), Barau FC (Kano)
Ana sa ran daga cikin ƙungiyoyi takwas da za su buga gasar, hudu ne kawai za su samu damar hawa matakin gasar Firimiyar Najeriya (NPFL). Haka kuma za a fitar da ƙungiya guda ɗaya a matsayin zakaran gasar NNL Super 8 na shekarar 2024/2025.
A cewar Ahmad Gwale, tawagar Barau FC na da kwarin gwiwa da jajircewa wajen samun nasarar da za ta kai su ga matakin gasar manya a Najeriya.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
