Connect with us

News

An Cafke Wani Fitaccen Dilan Ƙwaya a Kano

Published

on

Wasu Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Babban Jami’in Hukumar NDLEA

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa, NDLEA, ta ce ta cafke wani matashi da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a yankin Fagge na jihar Kano.

Advertisements
Advertisements

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad Maigatari, ya shaida a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi cewa an kama wanda ake zargin, Faisal Yusuf Umar, mai shekaru 23, ne bayan wani bincike da aka gudanar bisa bayanan da al’umma suka bayar.

Advertisements

Gidan Rediyo Ya Dakatar Da Babban Darakta Kan Sukar Gwamna

Maigatari ya ce jami’an NDLEA na reshen Fagge sun kai samame a ranar 18 ga watan Yuli a gidan wanda ake zargin da ke unguwar Dandali, inda suka gano kwalabe 40 na maganin tari Benylin mai ɗauke da Codeine (kimanin kilo 4), da kuma kuɗi naira 204,000 da ake zargin sun fito daga saida miyagun ƙwayoyin.

Advertisements
Advertisements

Hukumar ta ce ana ci gaba da bincike kafin gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending