Connect with us

News

Sojojin Sama Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592 A Borno Cikin Wata Takwas

Published

on

Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto 

Rundunar Sojin Saman Nijeriya (NAF) ta bayyana cewa ta kashe aƙalla ‘yan ta’adda 592 tare da lalata kayan aikin abokan gaba 372 a hare-haren sama da ta gudanar a Jihar Borno cikin watanni takwas da suka gabata.

Mai magana da yawun rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce hare-haren — waɗanda suka haɗa da tashin jiragen yaƙi sau 798, da jimillar sa’o’i 1,500 a sararin sama — sun rage ƙarfin mayakan Boko Haram da ISWAP a yankin Arewa maso Gabashin ƙasar.

Advertisement

Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Jami’an Tsaro Damar Kada Kuri’a Kafin Ranar Zaɓe

Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar, ya bayyana haka ne yayin ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a Maiduguri, ranar Talata.

A cewar Abubakar, rundunar ta yi amfani da jiragen yaƙi da helikwafta wajen kai hare-haren daga Gonori zuwa Rann, Dikwa, Damboa, Azir har zuwa Mallam Fatori, ba tare da gushewa ba. Ya ce an lalata motocin ‘yan ta’adda 206 da wuraren haɗa abubuwan fashewa 166.

Advertisement

“Yaƙinmu na sama a bana ya fi ƙarfi da inganci. Muna kashe manyan kwamandojin ‘yan ta’adda da lalata ababen zirgazirgarsu, tare da tabbatar da tsaron fararen hula da dawo da kwarin gwiwar jama’a,” in ji shi.

Abubakar ya kuma yaba wa shirin gwamnatin Borno na haɗin kai da al’umma wajen yaƙi da ta’addanci, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen samun nasara a fagen daga.

Advertisement

A nasa jawabin, Gwamna Zulum ya gode wa sojojin sama kan gudummawar da suke bayarwa, tare da kira da su ƙara ƙaimi wajen murƙushe ‘yan ta’adda a jihar.

 

Advertisement

TRT GLOBAL 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending