Connect with us

News

’Yan Bindiga Sun Yi Ajalin Mutum 7, Sun Jikkata 11 A Sabon Hari A Kaduna

Published

on

IMG 20250907 WA0030

Aƙalla mutum bakwai ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu 11 suka jikkata a wani sabon hari da ’yan bindiga suka kai ƙauyen Wake da ke gundumar Agunu, a Ƙaramar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:55 na safiyar Lahadi, lokacin da ’yan bindigar suka mamaye garin tare da yin ta’adi da harbe-harbe ba kakkautawa.

Advertisement

Farashin Kayan Abinci Ya Sauka A Kasuwanni, Amma Masu Dafa Abinci Sun Ki Rage Kuɗi —Rahoto

Bayan kashe mutum bakwai da jikkata wasu, maharan sun kuma yi garkuwa da wasu mazauna garin, duk da cewa adadin mutanen da aka sace bai bayyana ba a halin yanzu.

Waɗanda suka rasa rayukansu a harin sun haɗa da Elisha Paul, Japhet Bitrus, Obadiah Joshua, Luka Augustine, Ishaya Paul, Bawa Bulus da Ezekiel Augustine.

Advertisement

Daga cikin waɗanda suka jikkata kuwa akwai Gideon Pius, Zachariah Anthony, Moses Christopher, Uhu Sunday, Christopher Ishaya Sunday, Elisha Ishaku, Clement Godday da Janet Godday, waɗanda aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa.

Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida cewa: “’Yan bindigar sun kashe mutum bakwai, sun jikkata da dama sannan suka yi garkuwa da wasu. Kullum cikin fargaba muke kwana.”

Advertisement

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ci tura, domin bai ɗaga kiran waya ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.

 

Advertisement

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending