News
Yan Bindiga Sun Bude Wa ‘Yan Zaman Makoki Wuta
Rundunar ’yan sandan Jihar Anambra, ta fara bincike kan kisan wasu mutum huɗu da ’yan bindiga suka yi lokacin da suke zaman makoki.
Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun buɗe wa masu makokin wuta ne a ranar Alhamis a garin Ogidi, da ke Ƙaramar Hukumar Idemili.
Masu Zuwa Daurin Aure 19 Sun Rasu Bayan Rushewar Gada A Zamfara
Harin ya yi sanadin mutuwar mutum huɗu tare da jikkata aƙalla mutum 15.
Kakakin rundunar, Tochukwu Ikenga, ya ce suna zargin harin ya shafi rikicin ƙungiyoyin asiri ne.
Ya ƙara da cewa jami’an tsaro da suka isa wajen sun gano harsasai 16, kuma za su yi amfani da su wajen bincike.
Ikenga, ya ce nan gaba za su sanar da jama’a abin da binciken nasu ya gano.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
