News
Masu Zuwa Daurin Aure 19 Sun Rasu Bayan Rushewar Gada A Zamfara
Aƙalla mutum 19 sun riga mu gidan gaskiya a wani mummunan hatsari da ya auku sakamakon rushewar tsohuwar gadar Gwalli da ke Fass, ƙaramar hukumar Gumi a Jihar Zamfara.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:45 na yammacin Asabar, lokacin da wata mota ɗauke da baƙin daurin aure ta yi ƙoƙarin ketarawa, sai gadar ta rushe, motar ta fada cikin ruwa.
Masu Zuwa Daurin Aure 19 Sun Rasu Bayan Rushewar Gada A Zamfara
Shaidu sun bayyana cewa maza, mata da yara suka rasa rayukansu a hatsarin.
Wani mazaunin garin Fass, Babangida Halifa Ibrahim, wanda ya ce ya rasa ’yan uwa a cikin hatsarin, ya tabbatar da cewa mutanen da suka mutu sun kai 19.
Rahotanni sun nuna cewa za a gudanar da jana’izar waɗanda suka mutu a safiyar Lahadi.
Gadar Gwalli, wadda ke haɗa al’ummomi kamar Gwalli, Yar Gusau da Fass, ta daɗe tana cikin mawuyacin hali. An taɓa gyaranta ne a zamanin tsohon gwamna Abdulaziz Yari, amma ruwan sama mai yawa ya lalata ta tun kusan shekaru bakwai da suka gabata.
Mazauna yankin sun bayyana cewa rushewar gadar ta jefa su cikin matsanancin hali musamman a lokacin damina, inda suke yawan fuskantar haɗarin ambaliyar ruwa yayin da suke ƙoƙarin ketarewa.
Sun ce hatsarin da ya auku ranar Asabar ya sake tabbatar da yadda jama’ar Zamfara ke rayuwa cikin barazana, duk da ikirarin gwamnati na cewa tana gyara ababen more rayuwa a yankunan karkara.
Da aka tuntubi mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Mustapha Jafaru Kaura, ya ce bai da cikakken bayani kan lamarin, amma ya yi alƙawarin tuntuɓar hukumomin da abin ya shafa. Sai dai daga bisani, bai sake amsa kiran waya don ƙarin bayani ba.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
