News
Gwamna Yusuf Ya Sauya Wa Kwamishinan Shari’a Ma’aikata
Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi sabbin canje-canje a majalisar Zartarwarsa.
Cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar yace an canja
Yadda Wasu Yan Nijeriya Suka Yi Kashin Ƙulli 116 Na Hodar Ibilis A Gaban Jami’an NDLEA
Bar. Haruna Isa Dederi – daga Shari’a zuwa Sufuri.
Bar. Mustapha Nuruddeen Muhammad – daga Shari’a zuwa Muhalli a matsayin Babban Sakatare.
Kwamishinan Harkokin Jin Kai ya koma ma’aikatarsa ta asali bayan rike Sufuri a wucin gadi.
Ya kuma ce Sauye-sauyen za su fara aiki ne daga Talata, 23/09/2025.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce wannan mataki zai ƙara inganci, daidaito da sakamako mai kyau ga al’ummar Kano.
Advertisements
