Sports
Jirgin Tawagar ‘Yan Wasan Super Eagles Ya Yi Saukar Gaggawa A Kasar Angola
Tawagar ‘yan wasan Nijeriya tayi saukar gaggawa a ƙasar Angola bayan fashewar gilashin jirginsu.
Lamarin ya faru da yammacin yau Asabar, inda rahotanni suka bayyana jirgin da ke ɗauke da tawagar ya yi saukar gaggawa a ƙasar Angola saboda fashewar gilashin taga.
An Kama Wani Mutum Bisa Zargin Sayar Da Ɗansa Mai Kwanaki Biyar Da Haihuwa Kan N1.5m
Kawo yanzu haka tawagar na kasar Angola, domin jiran wani jirgin daga Najeriya ya zo daukar su domin dawowa.
Najeriya dai na shirin buga wasa da kasar Benin a mako mai zuwa, a wasan share fagen shiga gasar cin kofin duniya.
