News
DA ƊUMI-ƊUMI: ’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Yi Awon Gaba Da Dabbobi A Shanono
Wasu ’yan bindiga sun sake kai hari a garin Faruruwa, da ke yankin ƙaramar hukumar Shanono a jihar Kano, inda suka kashe mutum ɗaya tare da yin awon gaba da dabbobin al’umma.
Rahotanni sun bayyana cewa maharan, waɗanda ake hasashen suna kan babura sama da guda 25, kowannensu ɗauke da mutum uku dauke da bindigogi
Shaidu sun ce maharan sun kai hari kan shagon waya, inda suka fasa shaguna suka kwashe wayoyi
Wani mazaunin yankin da ya shaida wa Premier Radio cewa al’ummar Faruruwa yanzu na cikin tsananin fargaba, suna kuma neman gaggawar taimakon jami’an tsaro domin kauce wa sake faruwar irin wannan mummunan lamari.
Hukumomin tsaro har yanzu ba su fitar da wata sanarwa kan harin ba,
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
