Connect with us

News

Kwamishinan Tsaro Na Gombe Kanal Abdullahi Bello Ya Rasu A Hatsarin Mota

Published

on

Commissioner

Gwamnatin Jihar Gombe ta shiga jimami bayan rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello mai ritaya, wanda ya rasu sakamakon hatsarin mota a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe a ranar Juma’a.

A cewar wata sanarwa da Darakta Janar na Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, marigayi Kwamishinan ya rasu tare da mai tsaronsa, Sajan Adamu Husaini, yayin da suke dawowa daga Maiduguri, Jihar Borno, bayan halartar taron shiyyar Arewa maso Gabas kan shirin “National Disarmament, Demobilization and Reintegration (DDR).”

Advertisement

Jami’an ’Yan Sanda Sun Kama Ɗalibi Da Ya soki Gwamnan Neja

Misilli ya ce Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya  bayyana marigayi Kanal Bello a matsayin jarumi mai cikakken kishin ƙasa, wanda ya yi aiki da sadaukarwa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron cikin gida a Gombe.

A halin yanzu, direban Kwamishinan na karɓar jinya bayan raunukan da ya samu a hatsarin.

Advertisement

Gwamnatin ta ce za a sanar da lokacin jana’izar marigayin da mai tsaronsa nan gaba kaɗan.

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending