News
Majalisar Dokokin Kano Na Shirin Gyara Dokar Da Ta Kafa Kotunan Shari’ar Musulunci
Majalisar dokokin jihar Kano ta fara aiki kan kudurin gyara dokar da ta kafa kotunan shari’ar Musulunci da kuma kotunan daukaka kara na addinin Musulunci, domin magance sarkakiyar da ake samu tsakanin hukuncen wadannan kotuna da na kotunan majistare.
An gabatar da kudurin ne ta hannun mataimakin kakakin majalisar, kuma dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Rimin Gado, Muhammad Bello Butu-Butu, wanda ya ce lokaci ya yi da za a sabunta dokar domin dacewa da tsarin shari’a na zamani.
Himma Radio 91.1FM Ta Dauki Nauyin Sanya Yara A Makaranta A Kano
A cewarsa, tun bayan kafa kotunan shari’ar Musulunci a jihar Kano a shekarar 2000, akwai wasu sassa da ba su samu cikakken tanadi a dokar ba, abin da ke haifar da ruɗani a wajen aiwatar da shari’o’i.
“Dole ne mu gyara dokar domin mu fayyace hurumin kotunan Musulunci da na majistare, domin kada a rika samun rikici ko rashin fahimta tsakanin su,” in ji Butu-Butu.
Ya kara da cewa dokar da ke tafiyar da kotun daukaka kara ta shari’ar Musulunci ta kai kusan shekaru 50 da samar da ita, don haka akwai bukatar sabunta ta domin ta dace da tsarin rayuwar yau da kullum.
A cewar rahoton wakilin Premier Rediyo a Kano, Kamal Umar Kurna, majalisar ta kuma bayyana cewa daga cikin gyaran da za ta yi, za ta bai wa bangaren sulhu muhimmanci, domin rage cinkoson da ake samu a kotuna da kuma jinkiri wajen yanke hukunci.
Majalisar ta ce yin hakan zai taimaka wajen ganin cewa wasu matsalolin ana warware su cikin lumana ta hanyar sasantawa, maimakon kai su kotu kai tsaye.
