Connect with us

News

Iran Ta Ce Za Ta Yi Hulda Da Amurka Ne Kawai Idan Ta Daina Goyon Bayan Isra’ila

Published

on

74597519 803

Jagoran addinin Islma a Iran Ayatollah Ali Khamenei, ya ce Tehran za ta yi la’akari da yin hulda da Amurka ne kawai idan ta daina goyon bayan Isra’ila, kana kuma ta janye dakarunta daga yankin Gabas ta Tsakiya, da daina tsoma baki a al’amuran yankin.

Khamenei ya fadi haka ne yayin taron dalibai a bikin cika shekaru 46 da mamaye ofishin jakadancin Amurka, a 1979 a Tehran babban birnin kasar.

Advertisement

Kalaman jagoran na zuwa ne bayan yakin kwanaki 12 ya barke a watan Yuni, sakamakon hare-haren Isra’ila ta kai kamn kan Iran, lamarin da ya jawo Washington ta shiga kai farmaki kan wuraren nukiliyar Iran. Rikicin ya dakatar da tattaunawar nukiliya da aka jima ana yi tsakanin Iran da Amurka.

Tun bayan cimma yarjejeniyar zaman lafiya a watan Yuni, Iran na cigaba da fama da takunkuman karayar tattalin arziki daga kasashen yammacin duniya, musamman tun bayan janyewar Amurka daga yarjejeniyar nukiliya a 2018. Majalisar Dinkin Duniya ta sake farfado da wasu takunkumin a watan Satumba, bayan Birtaniya da Faransa da Jamus suka safe farfado da tsarin.

Advertisement

A nasa bangaren, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce a shirye su ke su koma teburin tattaunawa da Washington amma kan batun Nukiliya kawai, babu batun da ya shafi mizanin makami mai linzami.

 

Advertisement

 

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending