Connect with us

News

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Published

on

Wani Jirgin Rundunar Sojin Saman Najeriya Ya Hallaka Mutane Da Dama A Sokoto 

Babban Hafsan Sojin Saman Nijeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya umarci kwamandojin rundunar da su ƙara tsananta hare-hare ta sama kan maɓoyar ‘yan bindiga a sassan ƙasar.

Aneke, ya bayyana haka ne yayin wani taro da ya jagoranta tare da manyan kwamandojin da ke kula da yaƙin da ake yi da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga.

Advertisement

‎Sojojin Amurka Sun Kammala Tsara Irin Farmakin Da Za Su Kawo Wa Najeriya  ‎

A taron, an tattauna sabbin dabarun da za a yi amfani da su wajen kai hare-hare, da kuma yadda rundunar za ta yi aiki tare da sauran hukumomin tsaro don samun nasara a yaƙin.

Sanarwar da rundunar sojin sama ta fitar bayan taron ta ce an cimma matsaya kan ƙarfafa haɗin kai tsakanin sojin sama, sojin ƙasa, da sauran hukumomin tsaro.

Advertisement

Wannan mataki ya biyo bayan mako guda da rantsar da sabbin hafsoshin tsaro da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi.

 

Advertisement

 

LEADSHIP HAUSA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending