Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Ɗaukar Ƴansanda 30,000

Published

on

Shugaban Najeriya ya bayar da umarnin a dauki yannanda 30,000 bayan sace-sacen mutanen da aka yi a kwanakin baya bayannan.

Ofishin Shugaban kasar Bola Tinubu, ya kuma sanar da cewa duk jami’an tsaron da ke kare manya masu fada aji a kasar a mayar da su sauran fagen daga domin su ji su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar.

Advertisement

‎Wata Amarya Ta Yi Alajin Angonta Kwanaki Uku Bayan Ɗaura Auren Su A Katsina  ‎

Wannan yunkurin ya zo ne bayan da yara 50 daga cikin fiye da 300 da aka sace a makarantar sakandire st Mary da ke jihar Neja suka kubuta daga hannun wadanda suka sace su.

Wakiliyar BBC ta ce an umarci makarantu a wasu sassan jihohin Najeriya da su rufe makarantun bayan sace sacen daliban da a ka yi a baya bayannan, sannan kuma bayan shafe mako guda a hannun masu satar mutane an sako mutum 38 da aka sace a wani coci a jiya Lahadi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending